Sun kaso kashi biyu
1. Sunnonin da za a firta da baki
(kauliyya)
2. Sunnonin da za a aikata da gabbai
(fi’íliyya)
Sunnonin da za a firta da
ba’ki sun kaso kashi goma
- Karatun surah bayan fatiha
Sunnah ne karanta surah a rakaóin farko bayan fatiha da ijma’in mallamai
(taruwan mallamai) haka kuma sunnah ne karanta surah a raka’oin karshe (raka’ah
uku da ta hudu)
DALILI (HUJJA)
Hadisin Abi qata’dah yace
manzan Allah (SAW) ya kasance yana karanta a raka’oin farko fatiha da surah
yana jiyar da mu ayah wani lokacin yana karantawa a raka’oin biyun karshe da
suratul fatiha.
Rawi (muslim 421, bukhari 759).
Amma karantun surah a
raka’a uku da ta hudu an samu ne a
hadisin Abi sa’idin lallai manzan Allah
(SAW) ya kasance yana karanta a raka’oin biyun farko na azahar ayoyi talatin
talatin sannan a biyun karshe da ayoyi goma sha biyar biyar.
Rawi (muslim 452)
- Zikiri cikin ruku’u
Allahumma laka raka’atu wa laka
aslamtu wa bika a’mantu qhasha’a laka sam’i wa basari wa mukki wa azmi wa asabi
Rawi (muslim 771, tirmizi 4371, Abu dawud 760)
·
Subhanaka Allahumma rabbana wa bi
hamdika Allahumma agfirli
Rawi (bukhari 247, muslim 484)
·
Subbuhun quddusun rabul mala’ikati wa
ruhh
Rawi (muslim 487)
·
Subhana zil jabaruti wal malakuti wal
kibriya’u wal azma
Rawi (Abu
dawud 873)
- Azikru baádal kiyam minal ruku’i wa ba’ada rabbana walakalhamdu (zikir bayan dagowa daga ruku’u da kuma bayan rabbana walakalhamdu)
Allahumma rabbana walakalhamdu
mil’assamawati wa mil’al ardi wa mil’a ma bainahuma wa mil’a ma shita min
shay’in baada ahlusana’i wal majdi a haqqu ma kalal abdi wa kulluna laka abdi
Allahumma la ma ni’a lima a’adaita wa la mu’udi lima mana’ata wa la yanfa’u zal
jadd minkal jadd
Rawi (muslim 477, Abu dawud 747)
·
Rabbana walakalhamdu hamdan kasiran
tayiban mubarakan fihi.
Rawi (bukhari 237, Abu dawud 770)
- Azzikru fissujud (zikiri cikin sujjada)
Allahumma laka sajadtu wa bika
a’mantu wa laka aslamtu sajada wajhi
lilazi qalaqahu wa sawwarahu wa shaqqa wa basaruhu tabarakallahu ahsanul
qa’liqina.
Rawi (muslim 771)
·
Subhanakallahumma rabbana wa bi
hamdika Allahumma agfirli
·
Sauran biyun cikin na ruku’u za a iya
yinsu a cikin sujjada (subbuhun quddusun ……………..)
·
(subhana zil jabaruti …………………..)
- Al’iksaru minad du’a fis sujjud (yawanta yin addu’a a cikin sujjada)
Da cewar sa annabi (SAW) amma a cikin yin sujjada ku
yawaita yin addua tabas za a karba muku. Annabi (SAW) ya kasance yana fada a
cikin sujjadar sa ‘’Allahumma agfirli
zanbi kullahu dikkahu wa jillahu wa awwalahu wa akhirahu wa alaniyyatahu wa
sirrahu’’
Rawi muslim 483
- Addua baina sajadataini
Allahumma agfirli warhamni wajbirni
wahdini warzuqni
Rawi (Abu Dawud 850, Tirmizi 284)
·
Rabigfirli Rabigfirli
Rawi (Abu Dawud 874)
- Assalatu ala nabiyyi ba’ada tashahudu auwal wal akhir (yi wa annabi salatu bayan tahiyar farko da na karshe)
RA’AYOYIN MALLAMAI
- Imam shafi’i da imam Ahmad sun tafi akan wajabci yi wa annabi sallati a tahiyar karshe. Da mutum zai bari bai yi sallah sa bai inganta ba. Dan cewar sa annabi (SAW) acikin hadisin da hakim da abu hatim suka rawaito acikin sahihansu (yaya za mu yi maka sallati acikin sallah).
- Imam abu hanifa da malik sun tafi akan cewa yi wa annabi sallati a tahiyar karshe sunnah ne. dan cewar sa annabi (SAW) bayan ya koyar da yanda za a yi tahiya sai yace idan ku ka aikata haka sallah ku ta cika. (wannan shine dalilin su cewar yin sallati acikin sallah sunnah ne).
TUNATARWA
Amma ra’ayin mallaman farko (Imam shafi’i da Imam Ahmad shine mafi rinjaye )
Ga daya daga cikin salatin Annabi (SAW)
Allahumma salli ala Muhammad wa ala ali Muhammad wa
barik ala Muhammad wa ala ali Muhammad kama barakta ala Ibrahim wa ala ali
Ibrahim innaka hamidun majid
- Addua ba’adu tashahud auwal wa tsani (yin addua bayan tahiyar farko da ta karshe)
Amma yin addua a tahiyar farko dan cewar annabi (SAW) idan kunyi zama
acikin kowane raka’a biyu ku ce (attahiya’atu lillah ………………………) sannan dayanku
ya yi zabi da addua da yake so, amma bayan tahiya ta biyu dan cewar sa annabi
(SAW) idan dayanku ya gama tahiya karshe ya nemi tsari daga wajen Allah akan abubuwa
guda hudu;
·
Min azabi jahannam (neman tsari daga
azaban wuta)
·
Min azabi kabari (neman tsari dage
azaban kabari)
·
Wa min fitnatil mahya wal mamat
(neman tsari daga fitina rayuwa da mutuwa)
·
Wa min sharri masihi dajjal (neman
tsari daga sharin dajjal)
Rawi (bukhari
192, muslim 588)
- Attaslimatu tsaniya (yin sallama ta biyu)
Hakika annabi (SAW) ya kasance yana sallama biyu. An samo hadisin daga
A’mir bin Sa’ad daga babansa y ace ni na ga annabi (SAW) yana sallama a gefen
dama da gefen hagu har ina ganin hasken kumatun sa. (muslim 582).
Ita kuma sallama ta farko wajibi ce ta biyu kuma sunnah ce. Ya tabbata
annabi (SAW) yana yin sallama kwaya daya. Aisha uwar muminai ta ce lallai annabi
(SAW) ya kasance yana sallama daya acikin sallah ta gabar fuskar sa sannan sai
ya karkata zuwa gefen dama kadan.
Rawi (Tirmizi 290)
TUNATARWA
Amma mallamai sun ce yana yin sallama dayanne a sallah nafila a gida
wannan shi ya kawo uwar muminai ta gani har ta fada. Amma maganar yin sallama
biyu shine mafi ingancin zance wanda sahabai sama da goma sha biyar suka kawo
riwayar. Ga sunnan su kamar haka;
1) Abdullahi
bin mas’ud
2) Sa’ad
bin Abi waqqas
3) Sahal
bin Sa’ad assa’idi
4) Wa’il
bi hujirin
5) Abu
musa alshari
6) Khuzaifatul
yamani
7) Ammaru
bin yasir
8) Abdullahi
bin Umar
9) Jabir
bin samura
10) Barra’u bin azib
11) Abu maliki ashari
12) Dalk bin aliyu
13) Aus bin Aus
14) Abu ramsa
15) Adiyu bin umaira
Ku duba littafin zadul ma’ad fi hadiyi khairul ibad na ibn qayim aljauziya mujjaladi na daya shafi na shasa’in da tara zuwa dari.
- Azzikr wa du’a ba’ada sallah (zikiri da addua bayan sallah)
Yin zikiri a bayan sallah ya tabbata cikin hadisai da dama daga cikinsu:
·
Duk wanda yayi subhanallah 33
alhamdulillah 33 allahu akbar 33 a karshen sallah ya cika ya cike na dari da
cewa la’ilaha ilallah wahdahu la sharika lahu lahul mulku wa lahul hamdu wa
huwa ala kulli shay’in kadir. Annabi (SAW) yace za a kankare zunuban sa ko sun
kai yawan kumfar teku
Rawi (muslim 597)
·
Annabi (SAW) ya kasance idan ya idar
da sallah yana cewa astagfirullah sau 3
allahumma anta sallam wa minka sallam tabarakta ya zal jalali wal ikram
·
An samo daga ukbar bin a’mir annabi
(SAW) ya umarce ni ina karanta falaki da
nasi karshen ko wace sallah
Rawi (Abu dawud 1523)
·
Wanda duk ya karanta ayatul kursiyyu
a karshen ko wace sallah ta wajibi ba abinda zai hana shi shiga aljannah sai
mutuwa
Rawi (Ibn sinni)
Amma addua bayan sallah suna da yawa amma ga daya daga
cikin su; (allahumma a’ini zikirika wa shukrika wa husni ibadatik)
Rawi (Abu dawud 1508)
MARKAZ
NA SALAFIYYA NGURU YOBE STATE MALLAM IDRIS IBRAHIM ASSALAFI NGURU (SHUGABAN
MARKAZ)
No comments:
Post a Comment