Muna Murna Da Ziyarar Da Aka Kawo Mana

Muna Godiya Da Farin Ciki Ga Duk Gudun Mawar Shawara Dag Zaku Iya Bamu,

Sai Munji Daga Gare ku.

Saturday, June 25, 2011

JUMA'AT KAREEM

Haqiqa;
Mafi Girman Haske-Ilimi.
Mafi Girman Duhu-Jahilci
Mafi Girman Kyauta-Afuwa
Mafi Kyawon Zance-Gaskiya
Mafi Munin Zance-Karya
Mafi Kusantowar Al'amari- Tashin Qiyama
Mafi Girman Arziki- Wadatar Zuci
Mafi Kyawun Hali-Kunya
Mafi Munin Hali-Kisan Kai
Mafi Kusanta ga Allah- Ibada
Mafi Kusanta ga Shaidan- Hassada
Mafi Kusanta ga Aljanna- Aikin Alkhairi
Mafi Kusanta ga Wuta- Aikata Sharri. Allah yasa mufi karfin Zukatammu.

MAKIRCIN SHAIDAN GA DANADAM (2)

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai
jinkai. Dukkan yabo da godiya na
Allah ne, Ubangijin halittu. Tsira da
amincin Allah su tabbata ga
mafificin halittu, Muhammadu dan
Abdullahi, sallallahu alaihi wasallam, tare da alayensa da
sahabbansa da duk wanda ya bi
tafarkinsu har zuwa ranar karshe.
Bayan haka, yau ga ci gaban
tattaunawar Manzon Allah,
sallallaahu alaihi wasallam da shaidan. Mun kwana daidai inda
Ma’aiki, sallallaahu alaihi wasallam, ya yi godiya ga Allah da Ya azurta
al’ummarsa kuma ya tsiyata shaidan. Daga nan:
Sai Iblis ya ce, “ba mai yiyuwa ba ne. Ina ka ga tsirar al’ummarka alhali ni ina raye zuwa lokaci abin
sani? Yaya za ka dinga farin ciki a
kan al’ummarka, alhali ni ina mai shiga cikin jikinsu da magudanar
jininsu da tsoka, kuma alhali su ba
sa ganina. Kai, wallahi na rantse da
Wanda Ya halicce ni kuma Ya
jinkirta min zuwa ranar tashi, sai na
hallakar da su gabaki dayan su. Jahilansu da malamansu. Wadanda
suka iya karatu da wadanda ba su
iya karatu ba. Da kuma masu bautar
Ubangiji, sai dai bayin Ubangiji
tsarkakakku. ” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to su wane ne tsarkakakku a wajen ka ?” Sai shaidan ya ce, “ya Muhammadu, yanzu ba ka san cewa duk wanda
yake kaunar duniya da dukiya ba ya
cikin tsarkakakkun bayin Allah
Madaukaki ba? Amma idan ka ga
mutum ba ya kaunar duniya, ba ya
kaunar dukiya kuma ba ya kaunar yabo balle a yabe shi, to hakika na
san wannan yana daga cikin bayin
Allah tsarkakakku. To wannan sai na
rabu da shi domin ya fi karfina.
Hakika idan bawa ya dawwama a
kan son dukiya da son a yabe shi kuma zuciyarsa ta ta’allaka sha’awe-sha’awen duniya, to hakika shi wannan ya tattare dukkan abin
da na siffanta maku.
“ Yanzu ya Muhammadu, ba ka san son dukiya na daga cikin manya-
manyan zunubai ba? Yanzu ya
Muhammadu, ba ka san cewa son
shugabanci yana daga cikin manya-
manyan zunubai ba? Ya
Muhammadu, ba ka san cewa ni ina da ’ya’ya dubu saba’in ba? Kuma kowane daya daga cikinsu yana da
rundunar shaidanu guda dubu
saba’in a karkashinsa? Akwai daga cikinsu wanda na
wakilta shi a kan tsofaffi, amma
matasa kuwa babu wani sabani
tsakanina da su. Amma kananan
yara kuwa sai shaidanu su dinga
wasa da su kamar yadda suka ga dama. Akwai daga cikinsu wanda
hakika na wakilta shi ga masu
bautar Ubangiji. Akwai daga cikinsu
wanda na wakilta shi ga masu
gudun duniya, suna kaiwa suna
komowa a tsakaninsu, kuma suna fitar da su daga wannan hali zuwa
wancan hali, daga wannan kofar
zuwa waccan kofar, har sai sun fitar
da su daga hanyoyi zuwa wadansu
hanyoyi. Ni kuma sai na bata musu
tsarkin aikinsu, alhali suna masu bautar Allah Madaukaki ba tare da
tsarkakewar aiki ba, alhali kuma su
ba su sani ba.
“ Yanzu ya Muhammadu, ba ka da labarin Barsisi mai ibada cikin
addinin Nasara, wanda ya shafe
shekara saba’in [70] yana tsarkake aikinsa saboda Ubangiji Madaukaki,
har sai da ta kai Allah Ya warkar da
marasa lafiya da addu’arsa, amma ban bar shi ya kai ba. Sai da na sa
shi ya yi zina kuma ya yi kisan kai,
kuma ya zama kafiri. Ai shi ne
wanda Ubangiji Ya ambace shi a
cikin Littafinsa Mabuwayi da fadinSa
cewa: ‘Cewar misalin shaidan ne a yayin da ya ce da dan Adam
kafirce’. A lokacin da ya kafirce, sai shaidan ya ce da shi. ‘To ni babu ni, babu kai, domin ni ina tsoron Allah,
Ubangijin halittu”. “Yanzu ya Muhammadu, ba ka san cewa dukkan karya daga gare ni
take ba? Kuma ni ne wanda ya fara
yin karya? Kuma ni ba ni da aboki
sai makaryaci, wanda ya yi
rantsuwar karya, to shi ne
masoyina. “ Ya Muhammadu, yanzu ba ka san ni ne wanda ya rantse wa Hauwa’u da Adamu da Allah a kan cewa ni
mai nasiha ne a gare su ba ? Kuma
rantsuwar karya ita ce take faranta
min zuciya. Giba da annamimanci
kuwa su ne kayan marmarina da
farin cikina. Shaidar karya kuwa ita ce sanyin idanuwana, kuma ita ce
abar yardata. Wanda ya yi
rantsuwar shirka kuwa to ya
kusanta, ya zama babban mai
zunubi ko da rantsuwar shirkar nan
sau daya ne kawai, kuma ko da gaskiya ya fada, domin kuwa
wanda ya saba wa harshensa da
rantsuwar shirka, to hakika an
haramta masa matarsa. Sannan
kuma ba za su gushe ba suna
mazinata, kuma suna hayyafa har zuwa ranar Alkiyama, sai sun
kasance ’ya’yan zina gabaki dayansu. Sai a shigar da su wuta
saboda kalma kwaya daya tak.
“ Ya Muhammadu, hakika daga cikin al’ummarka akwai wanda yake jinkirta sallah daga lokacinta zuwa
wani lokacin. A duk yayin da yake
so ya mike zuwa sallah sai na tsare
shi ina yi masa waswasi, kuma sai
na ce da shi ‘akwai sauran lokaci, ba ka karasa abin da yake gabanka ba ’, har dai ya jinkirta sallah ya yi ta ba
a kan lokacinta ba. Sai a nannade
masa sallarsa a maka masa ita a
fuskarsa. Idan na ga zai rinjaye ni,
ya yi ta a kan lokacinta, sai na aiko
masa da wani daga cikin shaidanun mutane, sai ya shagaltar da shi har
lokacinta ya wuce. Idan kuma ya
rijaye ni a kan wannan, sai na kyale
shi har sai ya fara yin sallar, sai na
dinga cewa da shi ‘dubi hagu, dubi dama’, to idan na ga haka, sai raina ya yi mini dadi, sai na shafi fuskarsa
kuma na tsotsi tsakanin idanunsa
sai na dinga cewa yanzu ka aikata
abin da har abada sallarka ba za ta
gyaru ba’. “Kuma ka sani, ya Muhammadu, wanda ya yi waiwaye a cikin
sallarsa, to Ubangiji zai sa a mako
masa sallarsa a fuska. Idan kuwa ya
rinjaye ni a cikin sallarsa ya zo ya yi
ta shi kadai, to sai na sa shi ya yi ta
a cikin gaggawa sai ya dinga dungura ta kamar yadda zakara
yake tsattsagar dawa, nan da nan
kamar koton kurciya. Idan kuwa ya
rinjaye ni har na ga zai yi sallah a
cikin jama’a, to ba kyale shi zan yi ba. Sai na daura masa linzami. Ina
mai daga kansa kafin liman ya
daga. Kuma ina mai sunkuyar da
kansa kafin liman ya sunkuya. Kai
kuma ka sani, ya Muhammadu, duk
wanda ya aikata haka to ba shi da sallah. Idan kuma ya rinjaye ni a
nan, to sai na umarce shi ya dinga
tantankwasa hannunsa alhali yana
cikin sallar. Wanda ya aikata haka
kuwa, ni yake yi wa tasbihi a cikin
sallarsa. Idan kuwa ya rinjaye ni a nan, to sai na yi masa busa a cikin
hancinsa, wacce take za ta sa shi ya
yi hamma a cikin sallarsa, idan bai
toshe bakinsa a yayin da yake
hammar ba, to sai in shiga cikin
bakinsa. To wannan sai ya kara masa son duniya da kaunarta. Sai
ya kasance ba ya sauraren kowa sai
ni, kuma ba ya biyayya ga kowa sai
ni.
“ Ya Muhammadu, ina aikin al’ummar taka yake? Ga ni ina umarnin talakawa, ina ce musu
sallah ba ta talakawa ba ce, ta
wadanda Allah Ya yi wa ni’ima ce. Kuma ina cewa da marar lafiya,
sallah ba wajibi ba ce a kan marasa
lafiya, sallah ta wadanda Allah Ya yi
wa ni’ima da lafiya ce. Ba ku ji Ubangiji Madaukaki yana cewa:
“Babu laifi ga marar lafiya” , idan kuwa sallah ta kubuce ma marar
lafiya har ya mutu, to hakika ya
mutu kafiri, idan kuwa ya mutu
yana tarikus-salat a yayin rashin
lafiyarsa to hakika zai sadu da
Ubangiji Yana mai fushi da shi. “ Ya Muhammadu, idan abubuwan da nake gaya maka karya ne, to roki
Ubangiji Ya maida ni toka. Ya
Muhammadu, yaya za ka yi farin ciki
a kan al’ummarka, alhali na kasance ina fitar da sudusin al’ummarka daga Musulunci?” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “ya kai la’antaccen Allah, wane ne abokin zaman ka?” Sai shaidan ya ce: “maciyin riba shi ne abokin zamana.” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to wane ne abokinka?” Sai shaidan ya ce “barawo shi ne abokina.” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to wane ne masoyinka?” Sai shaidan ya ce, “Tarikus-Salat (wato mai barin sallah) shi ne
masoyina.” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “ya la’antaccen Allah, to mene ne yake karya doron bayanka?” Sai shaidan ya ce, “kururuwar doki a wajen daukaka kalmar Allah. ” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to mene ne yake narkar da jininka ?” Sai shaidan ya ce, “tuban mai tuba, shi ne yake narkar da ni.”

Wednesday, June 22, 2011

Ma’ana da illolin zina da luwadi damadigo da kuma hukuncinsu

Ya tabbata a cikin hadisi an tambayi Annabi (S.A.W) a kan wane zunubi ne ya fi girma, sai Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Shirka da Allah alhali Shi ne Ya halicce ka.” Sai aka ce ‘sai wane?’ Sai ya ce, “Sannan kashe danka don kada ya ci tare da kai.” Sai aka ce “sannan sai wane?” Sai ya ce, “Ka yi zina da matar makwabcinka.” (Bukhari).
Allah Madaukakin sarki Ya sanya hukuncin wanda duk ya yi zina kuma ya taba aure, a jefe shi, namiji ko mace; idan kuwa bai taba aure ba, sai a yi masa bulala dari, sannan a bakuntar da shi a wani gari daban tsawon shekara guda.
Duk wanda ya kalli hukuncin zina, zai ga Allah Ya kebance shi da wasu abubuwa masu yawa, saboda munin zina. Ga kadan daga cikin abubuwan da hukuncin ya kunsa:
•Kausasawa wajen ukubar mazinaci, ta hanyar jefewa. Ko kuma bulala da bakuntarwa shekara guda.
•Hana jin tausayin mazinaci ko mazinaciya yayin da ake musu ukuba. Allah Ya ce :
“Mazinaciya da mazinaci ku yi wa kowane daya daga cikinsu bulala dari. Kada ku ji tausayinsu a cikin addinin Allah, in dai kun yi imani da Allah da ranar karshe” . (Annur : 2).
•Yi musu ukuba a gaban mutane, ba a yarda a yi musu a boye ba, Allah Ya ce :
“Wasu bangare na muminai su halarci wajen yi musu ukuba (haddi)”. (Annur :2).
Duk wadannan abubuwa suna nuna mana munin zina da rashin kyanta a Musulunci. Imamul Bukhari ya kawo, a cikin ingantaccen littafinsa, daga Maimun Al-audiy ya ce, “A lokacin jahiliyya na taba ganin wani biri da ya yi zina da wata biranya, sai sauran biran suka taru suka jefe su”.
Mafi munin zina ita ce wadda mutum zai yi da mahaifiyarsa, sai da muharramarsa, sai wadda zai yi da matar makwabcinsa. Allah Ya kare mu.
Illolin Zina: Babu ko shakka duk mai hankali ya san cewa zina tana tattare da illoli masu yawa, wadanda suke shafar mazinacin ko mazinaciyar, ko su shafi al’umma gaba daya. Ga wasu daga cikin illolinta :
1. Zubar da mutunci da jawo wa kai kaskanci: Duk matar da ta yi zina to ta jawo wa kanta da danginta da mijinta kaskanci, ta kuma zubar musu da mutunci a idon duniya. Idan har ta sami ciki ta haihu, sannan ta kashe dan, to ta hada laifi biyu, laifin zina da laifin kisan kai. In kuma ta bar shi, to kuma ta shigar wa mijinta ko danginta, wanda ba ya cikinsu. Idan kuwa mai zinar namiji ne to ya lalata mace, ya jawo mata lalacewa da tabewa, wanda hakan lalata duniya ne
gaba daya.
2. Zina ta hada dukkan sharri gaba daya: Saboda a cikin zina akwai rashin tsoron Allah; rashin kunya; rashin tsantseni; rashin cika alkawari; karya da butulci da sauransu. Duk kuwa wadannan munanan halaye a Musulunci. Ta’aliki: Mukalar kalmomin “Taala” da “Amin” a sallama Daga Alhaji Ahmad Muhammadil’Amin (Bawalle)
Dukkan godiya da yabo suna kara tabbatuwa ga aninihin Mai su, Ubangiji, kuma makagin kowa da komai ALLAH – Tabaraka wata’ala. Mahallicin mutum Ya sanar da shi (mutun) abin da bai sani ba. Dadin tsiran amincin Allah su ci gaba da karuwa ga mafificin halitta, shugaban dukkan Annabawa da Manzanni tare da zuri’arsa tsarkaka bai daya.
A ranar Juma’a 18 ga Muharram 1432, ina ofishina a Ma’ahd, wani dalibi ya zo min da jaridar Aminiya, ya ce “ga jaridar nan, lallai tunda marubucin ya nemi a shiryar da shi, baccin an karanta makalarsa, to ka yi rubutu a kai, kuma wannan maudu’in ya zama shi za ka yi mana ta’liki a ranar Laraba a ma’ahd domin tahdib.” Sai na ce tun da a kan shak’wa ce ilmiyyah, zan rubuta – in Allah (TWT) Ya so - domin na ga shi marubucin na magana ne a kan hujja kuma ai kowa ya san cewa HUJJA MAKAMIN AHLIL – ZIKR ne.
Mai karatu karimi, ina farawa da jawo hankalin duk wanda zai yi jawabi da sunan Musulunci, to, ya yi taka-tsan- tsan, ya ga cewa Zatin Allah ya nufa, kana da tawali’u irin na marubucin a makalarsa. Hujjojinsa su zama daga kitabu, sunnah, babu gociya, baudiya ko kwana, balle fadin son rai don wata manufa tasa, saboda hadarin da ke tattare da yi hakan.
Shi kuma mai hadisi, ijtihadinsa, in ya yi sawaba, ajraini, in kuwa akasin haka, ajrun wahid. Amin. Sai dai na ji dadin fahimtar cewa marubucin makalar ba yana jayayyar daukakar Allah ba ne, ko kuma bai yarda sallama ba fatan alheri ce ba, la la, shi dai a gurinshi ba su da mazauni, gurin yin sallamar ko amsawa. To wannan matsalar ba karama ce ba, tana da fadin gaske, zan raba ta kashi biyu insha’Allah (TWT). Na farko nunasshe da shi cewa duk hujjojinsa na Hadisai 5 ba su tsaya a kan yadda ake yin sallama da mayar da ita kawai ba. Kuma, kamar yadda ya nemi tabbatattun hujjoji na yiwuwar a saka kalmomin, to ga nema a gare shi ta hanyar tambayar - shin in Annabi bai yi ba, yana hukunta cewa kada a yi wani aikin ne? Amsa ita ce, Annabi bai yi ba, ba hujja ba ce, Annabi ya hana, ita ce hujja. Kash, sai ga shi M. Ahmad bai taimaka wa dalibai irinmu da Hadisi
ko da rarruana ne inda Ma’aiki ya hana a ce “Ta’ ala” ko “Amin”, a mas’alar sallama.
Ke nan za mu fahimci cewa yin abu a da’irar Islama yana zama muhdatha ce in har ba ya cikin Ayyukan Islama, amman ko da Annabi bai yi ba, shari’ar Islama ta tabbatar da samun sararin yi a Ayyukan Ibadan.
Misali:- Ingantaccen Hadisin da Imam Muslim ya ruwaito a Kitabus salati, Babu fadlul Duhuri Billail wan-nahar/ wa fadlul Duhuri Ba’dal Wudu’i (Hadith na 1149) da sahihih Muslim Babu Min Fadlul Bilal (Hadith 6,609) inda suka tabbatar cewa Annabi (S.A.W) bai yi wani aiki ba, amman sai ga shi Bila Babban Bawa, ya bai wa Ma’aiki amsa cewa shi a duk lokacin da ya dawwama da tsarki, in har yana da alwala, sai ya yi nafila raka’a biyu. Annabi bai ce masa me ya sa ka yi abin
da ban yi ba, kuma ban sa ka ba. Sai kawai ya tabbatar cewa yana jin motsin takalmin Bilal a gabanshi, a aljanna.

MAKIRCIN SHAIDAN GA DAN ADAM

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai
jinkai. Dukkan yabo da godiya na
Allah ne, Ubangijin halittu. Tsira da
amincin Allah su tabbata ga
mafificin halittu, Muhammadu dan
Abdullahi, sallallahu alaihi wasallam, tare da alayensa da
sahabbansa da duk wanda ya bi
tafarkinsu har zuwa ranar karshe.
Bayan haka, a yau da yardar Allah,
ina son yin fadakarwa ne a kan irin
makircin da shaidan ke yi wa dan Adam, a lokacin da yake a raye ko
kuma a lokacin da ya zo mutuwa.
Ya Allah Ka sallada mu a kan
shaidan la’antacce, kuma Ka shiga
tsakaninmu da shi. Amin.
To ya ’yan uwa musulmi, kamar yadda muka sani ne, Allah SWT Ya
ba shaidan damar shiga kowane
bangare na jikin dan Adam, jini da
tsoka da kuma bargo, inda ta kai
har yana lalata imanin mutum, ya
lalata sallar mutum. Yana fitar da kai daga imaninka. Shin mun manta
ne cewa wata rana Allah SWT Ya
taba umartar shaidan da cewa ya je
gurin Manzon Allah, sallallaahu
alaihi wasallam, ya amsa masa
dukkan tambayoyin da zai masa? Abdullahi dan Abbas [RA] ya ce,
“wata rana mun kasance tare da
Manzon Allah, sallallaahu alaihi
wasallam, a cikin wani daya daga
cikin gidajen mutanen Madina, tare
da jama’a, sai muka ji wani mai kira yana kira cewa: “ya ku mutanen
gidan nan ku zo ku yi min iznin
shigowa, domin na tabbata kuna da
bukata a gare ni.” Sai Manzon Allah,
sallallaahu alaihi wasallam, ya ce,
“ko kun san wane ne mai maganar nan?”
Sai sahabbai suka ce, “Allah da
ManzonSa kadai suka sani.” Sai
Annabi ya ce, “Iblis la’antaccen
Allah ne, Allah Ya kara la’antarsa.
Amin.” Sai Umaru dan Khaddabi (RA) ya ce “ya Manzon Allah ko za ka
yi mini izini in kashe shi?” Sai
Manzon Allah, sallallaahu alaihi
wasallam, ya ce “sannu dai ya
Umar, yanzu ba ku san shi shaidan
yana daga cikin wadanda aka saurara wa ba har zuwa lokaci abin
sani? Sai dai ku je ku bude masa
kofa, domin kuwa shi umarninsa
aka yi domin ku fahimci abubuwan
da zai fada muku.”
dan Abbas (RA) ya ce, “sai kuwa aka bude masa. Shigowarsa ke da wuya
sai muka gan shi tsoho ne mai ido
daya, a gemunsa akwai ’yan gasu
irin na doki. Idanunsa kuwa kamar
na alade, labbansa kuwa kamar na
bajimin sa, sai ya ce: ‘Assalamu Alaikum, ya Muhammadu. Assalamu
Alaikum ya jama’atal muslimina’.
Sai Manzon Allah SAW ya ce,
“Aminci ya tabbata ga Allah, ya kai
La’antacce. Kai dai fadi abin da ya
kawo ka da kuma bukatarka.” Sai Iblis ya ce: “ya Muhammadu,
wannan zuwan ba zuwan kaina ba
ne, na zo ne a kan wata bukata.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “wace
bukata ce ta kawo ka, ya
La’antacce?” Sai Iblis ya ce: “wani mala’aika ya
zo daga Ubangiji Mai Girma, ya ce
‘hakika Ubangiji Madaukaki Yana
umarnin ka da ka je zuwa ga
Muhammadu SAW kana
wulakantacce kuma kana mai kaskastar da kai a gare shi, domin
ka ba shi labarin irin yadda kake
shirya wa dan Adam makirci da
kuma yadda kake hallakar da shi.
Kuma ka gaya masa gaskiya a cikin
duk irin abubuwan da ya tambaye ka. Na rantse da buwayaTa da
daukakaTa, idan ka kuskura ka yi
masa karya guda daya tak, ko kuma
ka ki gaya masa gaskiya, to ka
tabbata Zan kona ka In maida kai
tokar da iska za ta yi dai-dai da ita a bayan kasa. Kuma In sanya
makiyanka su yi maka dariyar
gamgamko.’ To hakika ga ni na zo
maka, ya Muhammadu, kamar
yadda aka umarce ni. Don haka, ya
Muhammadu ka tambayi duk abin da kake so, zan gaya maka gaskiya,
domin idan ban gaya maka gaskiya
ba, to hakika makiyana za su yi mini
dariya. Ni kuma babu abin da na ki
jini a duniya irin dariyar makiyi.”
Manzon Allah SAW ya ce: “Ya Iblis idan ka kasance kai mai gaskiya ne,
to ka ba ni labari wane ne farkon
makiyinka?”
Sai Iblis ya ce, “Muhammadu ai kai
ne babban makiyina a cikin bayin
Allah da kuma duk wanda yake kwaikwayonka Muhammadu.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce:
“sannan kuma sai wa ka fi ki Iblis?”
Sai shaidan ya ce, “sai kuma saurayi
mai tsoron Allah, wanda ya mika
kansa wajen bautar Allah Madaukaki.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce:
“sannan kuma sai wa?”
Sai Iblis ya ce, “sannan malami mai
tsantseni. Kuma a wani lokaci shi
mai tsoron Allah ne.” Sai Manzon Allah SAW ya ce,
“sannan kuma sai wa ka fi ki?”
Sai Iblis ya ce, “sai malamin da yake
dauwama a cikin tsarki har sau
uku.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “sannan kuma sai wa?”
Sai Iblis ya ce, “sannan kuma sai
talaka mai yawan hakuri matukar
bai kai karar cutarsa ba.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “yaya
aka yi ka san cewa shi mai hakuri ne?”
Sai Iblis ya ce, “ya Muhammadu, ai
idan ya kai kara a halin da yake ciki
ga wani mutum irinsa har kwana
uku to ba za a rubuta masa ladar
masu hakuri ba.” Sai Manzon Allah SAW yace, “sannan
kuma sai wa?”
Sai Iblis ya ce, “sannan kuma
mawadaci mai yawan godiya.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “yaya
aka yi ka san cewa shi mawadacin mai yawan godiya ne?”
Sai Iblis ya ce, “idan na ga
mawadaci yana riko da halali kuma
yana ajiye shi a inda ya dace.”
Sai Manzon Allah SAW ya ci gaba da
tambayar shaidan, “To yaya kake samun kanka idan al’ummata suka
tashi zuwa Sallah?”
Sai shaidan ya ce: “ya Muhammadu
idan al’ummarka suka tashi zuwa
Sallah, sai zazzabi ya kama ni da
masassara.” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to
idan suka dauki azumi fa?”
Sai Iblis ya ce, “sai a daddaure ni
har sanda suka sauke azuminsu.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to
idan kuma suna aikin Hajji fa?” Sai Iblis ya ce, “idan suna aikin hajji
sai a haukatar da ni.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “idan
suna karatun Alkur’ani fa?”
Sai Iblis ya ce, “sai a narkar da ni,
kamar yadda ake narkar da darma a cikin wuta.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to
idan suka yi sadaka fa?”
Sai Iblis ya ce, “sai in ji kamar mai
sadakar nan ya dauki zarto ya raba
ni gida biyu.” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “me ya
kawo haka, ya aba marrata?”
Sai Iblis ya ce, “domin a cikin
sadaka akwai kyawawan abubuwa
guda hudu:
1. Hakika mai sadaka Allah Madaukaki Yana saukar masa da
albarka a cikin dukiyarsa.
2. Kuma Yana soyar da shi a wajen
bayinSa.
3. Kuma Yana sanya sadakarsa ta
zama hijabi tsakaninsa da wuta. 4. Kuma Ubangiji Yana yaye masa
talauci da masifu.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to me
kake cewa a kan Abubakar?”
Sai Iblis ya ce, “ya Muhammadu, ai
Abubakar bai bi ni ba a lokacin Jahiliyya. Yaya zai bi ni a wannan
zamani?”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to me
kake cewa a kan Umar?”
Sai Iblis ya ce, “ai ban taba cin karo
da Umar ba face sai na yi ta kaina.” Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to me
kake cewa a kan Usman?”
Sai Iblis ya ce, “ina jin kunyar
wanda mala’ikun Ubangiji suke jin
kunyarsa.”
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “to me kake cewa a kan Aliyu?”
Sai Iblis ya ce, “kaicona, ina ma na
rabu da shi , shi kuma ya rabu da ni.
Amma ina! bai yarda da haka ba.
Sai Manzon Allah SAW ya ce, “na
gode wa Allah da Ya azurta al’ummata, kai kuma Ya tsiyataka,
har zuwa ranar Alkiyama.”

Tuesday, June 21, 2011

Manufofin Wannan Shafi

Assalamu Alaikum mai karatu wannan an samar da shi don jin dadin ma'abota karatun kimiyya da fasaha ta yanar gizo,